Innalillahi Wa’Inna’ilaihi Raji’un Wasu Yan Bindiga Sun Kashe Mutane (30) A Jihar Arewa Maso Gabas Borno – Interestingasf

Yanzu yanzu muke samun labari daga jihar borno maiduguri dangane da harin kungiyar boko haram takai musu a sansanin ‘yan gudun hijira dake Dikwa, Inda Ake Zargin Sun Kashe Mutane Kimanin sama da (30) Talatin a cikin sansanin.

Hukumar kula da sansanin ‘yan gudun hijira ta jihar borno ta bayyana wannan lamari daya faru da mutanan a jiya laraba ansamu Hotunan gawarwakin mutanan da aka kashe amma babu kyawun gani.

Gwamnan jihar ta maiduguri babagana umara zulum jajirtaccen gwamna a arewa ya bada umarnin a tsaurara bincike dangane da wannan lamari daya faru na kisan mutanan a cikin sansanin su na yan gudun hijira domin magance matsalar tsaron yankin cewar babagana zulum.

Hakika jihar borno ta kasance daya daga cikin manyan jihohin arewa a nigeria saidai kuma jihar tanakan gaba wurin samun matsalar rashin ingantaccen tsaro daga wurin gwamnatin tarayya domin itama yakamata tana taimaka mana da magance matsalar tsaro a jihar ta Maiduguri.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *