Yanzu yanzu yadda sakamakon zabe ya nuna na jihar katsina sun fitar da sanarwar yadda tsohon mataimakin shugaban kasar nigeria alhaji atiku abubakar ya lashe zaben wannan shekakar a jihar ta katsina.

Tsohon mataimakin shugaban kasar nigeria alhaji atiku abubakar yayi nasarar samun rinjayen kuri’u mafiya yawan gaske a cikin zaben wannan shekarar na (2023) karkashin jam’iyyar (PDP) na jihar katsina.
Yayin da tsohon mataimakin shugaban kasar atiku abubakar ya kayar da Bola Ahmed Tinubu na jam’iyyar (APC) a cikin jihar ta katsina yanzu dai haka alhaji atiku abubakar shine yake kan gaba wurin samun nasarori a wasu jihohin na arewa.
Saidai kuma idan aka hade yawan kuri’un yan takarar wanda yake akan gaba ba kowa bane banda dan jam’iyyar hamayya wato Bola Ahmed Tinubu na jam’iyyar ta (APC) cikin wannan shekara saidai muce allah ubangiji yayi mana zabi na alkhairi.